All Islam Library
1

Ba Mu bũɗa maka zũciyarka ba (dõmin ɗaukar haƙuri da fahimta)?

2

Kuma Muka saryar maka da nauyinka, Ashe.

3

Wanda ya nauyayi bãyanka?

4

Kuma Muka ɗaukaka maka ambatonka?

5

To, lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.

6

Lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.

7

Sabõda haka idan ka ƙãre (ibãda) sai ka kafu (kana rõƙon Allah).

8

Kuma zuwa ga Ubangijinka ka yi kwaɗayi.