1
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
2
Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;
3
Mai rahama, Mai jin ƙai;
4
Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.
5
Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.
6
Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.
7
Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.