All Islam Library
1

Inã rantsuwa da hantsi.

2

Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).

3

Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.

4

Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.

5

Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.

6

Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?

7

Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?

8

Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?

9

Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.

10

Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.

11

Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).