All Islam Library

90 - The City - Al-Balad

:1

Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.

:2

Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.

:3

Da mahaifi da abin da ya haifa.

:4

Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.

:5

Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?

:6

Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"

:7

Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?

:8

Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?

:9

Da harshe, da leɓɓa biyu.

:10

Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?

:11

To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?

:12

Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?

:13

Ita ce fansar wuyan bãwa.

:14

Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.

:15

Ga marãya ma'abũcin zumunta.

:16

Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.

:17

Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.

:18

Waɗannan ne ma'abũta albarka

:19

Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci

:20

A kansu akwai wata wuta abar kullewa.