All Islam Library

91 - The Sun - Ash-Shams

:1

Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.

:2

Kuma da wata idan ya bi ta.

:3

Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.

:4

Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.

:5

Da sama da abin da ya gina ta.

:6

Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.

:7

Da rai da abin da ya daidaita shi.

:8

Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.

:9

Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.

:10

Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.

:11

Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.

:12

A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).

:13

Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"

:14

Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).

:15

Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).