All Islam Library

80 - He Frowned - `Abasa

:1

Yã game huska kuma ya jũya bãya.

:2

Sabõda makãho yã je masa.

:3

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

:4

Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

:5

Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

:6

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

:7

To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

:8

Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

:9

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

:10

Kai kuma kã shagala ga barinsa!

:11

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

:12

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

:13

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

:14

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

:15

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

:16

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

:17

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

:18

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

:19

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

:20

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

:21

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

:22

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

:23

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

:24

To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

:25

Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

:26

Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

:27

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

:28

Da inabi da ciyãwa.

:29

Da zaitũni da itãcen dabĩno.

:30

Da lambuna, mãsu yawan itãce.

:31

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

:32

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

:33

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

:34

Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

:35

Da uwarsa da ubansa.

:36

Da mãtarsa da ɗiyansa.

:37

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

:38

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

:39

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

:40

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

:41

Baƙi zai rufe su.

:42

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).