All Islam Library

79 - Those who drag forth - An-Nāzi`āt

:1

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

:2

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

:3

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

:4

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

:5

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

:6

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

:7

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

:8

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

:9

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

:10

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

:11

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

:12

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

:13

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

:14

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

:15

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

:16

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

:17

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

:18

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

:19

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

:20

Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

:21

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

:22

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

:23

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

:24

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

:25

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

:26

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

:27

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

:28

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

:29

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

:30

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

:31

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

:32

Da duwatsu, Yã kafe ta.

:33

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

:34

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

:35

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

:36

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

:37

To, amma wanda ya yi girman kai.

:38

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

:39

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

:40

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

:41

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

:42

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

:43

Me ya haɗã ka da ambatonta?

:44

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

:45

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

:46

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.