All Islam Library

78 - The Tidings - An-Naba

:1

A kan mẽ suke tambayar jũna?

:2

A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?

:3

Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?

:4

A'aha! Zã su sani.

:5

Kuma, a'aha! Zã su sani.

:6

Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?

:7

Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?

:8

Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?

:9

Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?

:10

Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

:11

Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?

:12

Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?

:13

Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?

:14

Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?

:15

Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?

:16

Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?

:17

Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.

:18

Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.

:19

Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.

:20

Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.

:21

Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.

:22

Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.

:23

Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.

:24

Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.

:25

Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.

:26

Sakamako mai dãcẽwa.

:27

Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.

:28

Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!

:29

Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.

:30

Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.

:31

Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

:32

Lambuna da inabõbi.

:33

Da cikakkun 'yammata, tsãrar jũna.

:34

Da hinjãlan giya cikakku.

:35

Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

:36

Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

:37

Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

:38

Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

:39

Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

:40

Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"