All Islam Library

81 - The Overthrowing - At-Takwīr

:1

Idan rãna aka shafe haskenta

:2

Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

:3

Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

:4

Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

:5

Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

:6

Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

:7

Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

:8

Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

:9

"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

:10

Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

:11

Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

:12

Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

:13

Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

:14

Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

:15

To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

:16

Mãsu gudu suna ɓũya.

:17

Da dare idan ya bãyar da bãya.

:18

Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

:19

Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

:20

Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

:21

Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

:22

Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

:23

Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

:24

Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

:25

Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

:26

Shin, a inã zã ku tafi?

:27

Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

:28

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

:29

Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.