All Islam Library

70 - The Ascending Stairways - Al-Ma`ārij

:1

Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.

:2

Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.

:3

Daga Allah Mai matãkala.

:4

Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.

:5

Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.

:6

Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.

:7

Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.

:8

Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.

:9

Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.

:10

Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.

:11

Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

:12

Da matarsa da ɗan'uwansa.

:13

Da danginsa, mãsu tattarã shi.

:14

Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

:15

A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

:16

Mai twãle fãtar goshi.

:17

Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

:18

Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

:19

Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

:20

Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

:21

Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

:22

Sai mãsu yin salla,

:23

Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

:24

Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

:25

Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

:26

Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

:27

Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

:28

Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

:29

Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

:30

Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

:31

To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

:32

Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

:33

Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

:34

Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

:35

Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

:36

Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).

:37

Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!

:38

Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?

:39

A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.

:40

Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.

:41

Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.

:42

Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).

:43

Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.

:44

Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)