All Islam Library

71 - Noah - Nūĥ

:1

Lalle ne Mun aiki Nũhu zuwa ga mutãnensa, cẽwa ka yi gargaɗi ga mutãnenka gabãnin wata azãba mai raɗaɗi ta zo musu.

:2

Ya ce: "Ya mutãnena ni, a gare ku, mai gargaɗi ne, mai bayyanãwa."

:3

"Cewa ku bauta wa Allah, ku ji tsõronSa, kuma ku bĩ ni."

:4

"Allah zai gãfarta muku daga zunubanku kuma Ya jinkirta muku zuwa ga ajalin da aka ambata. Lalle ne ajalin Allah idan ya zo, ba za a jinkirta Shi ba, dã kun kasance masana (ga abin da nake faɗã dã, kun bar kãfirci)."

:5

Nũhu) ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne, na kirãyi mutãnena, a cikin dare da yini."

:6

"To, amma kirana bai ƙãre su ba sai da, gudu (daga gare ni)."

:7

"Kuma lalle ne ni, kõ da yaushe na kirãye su dõmin Ka gãfarta musu, sai su sanya yatsunsu a cikin kunnuwansu, su lulluɓe da tufãfinsu, su dõge ga yin laifi. Sun yi girman kai iyãkar girman kai."

:8

"Sa'an nan lalle ne ni, na kira su, a bayyane."

:9

"Sa'an nan lalle ne, na yi yẽkuwa sabõda su, kuma na gãna da su a cikin asĩri."

:10

"Shi na ce, 'Ku nẽmi gãfara daga Ubangijinku, lalle ne shi Ya kasance Mai gãfara ne."

:11

"Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ɓuɓɓuga."

:12

"Kuma ya yalwata muku game da dũkiya da ɗiya, Ya sanya muku (albarka) ga gõnaki, kuma Ya sanya muku koguna."

:13

"Me ya sãme ku, bã ku fãtar sãmun natsuwa daga Allah,"

:14

"Alhãli kuwa, lalle ne, Ya halitta. ku, a cikin hãlãye?"

:15

"Ba ku ga yadda Allah Ya halitta wasu sammai bakwai ɗabaƙõƙĩ a kan jũna ba?"

:16

"Ya sanya watã a cikinsu, yana mai haske, Ya sanya rãnã babbar fitila?"

:17

"Kuma Allah Ya tsirar da ku daga ƙasa (kamar ganye) tsirarwa."

:18

"Sa'an nan Ya mayar da ku a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitarwa."

:19

"Kuma Allah Ya sanya muku ƙasa shimfidaɗɗiya."

:20

"Dõmin ku shiga a cikinta, hanyõyi mãsu fãɗi."

:21

Nũhu ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne sũ sun saɓa mini sun bi wanda dukiyarsa da ɗiyansa ba su ƙãre shi da kõme ba sai da hasãra."

:22

"Kuma sun yi wani mãkirci, mãkirci babba."

:23

"Kuma suka ce: Faufau kada ku bar gumãkanku, kuma faufau, kada ku bar wadda, kuma kada ku bar suwã kuma kada ku bar Yagũsa da Ya'ũƙa da Nasra."

:24

"Kuma lalle ne sun ɓatar da (mutãne) mãsu yawa, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai (kõme) sai ɓata."

:25

Sabõda laifukansu na ganganci aka nutsar da su, sa'an nan aka sanya su a wuta. Saboda haka ba su sãmã wa kansu wani mataimaki wanin Allah ba.

:26

Kuma Nũhu ya ce: "Ya Ublngijina! Kada Ka bari, a kan ƙasa, daga cikin kãfirai, wanda ke zama a cikin gida."

:27

"Lalle ne, Kai idan Ka bar su, zã su ɓatar da bãyinKa, kuma bã zã su haifi kowa ba fãce fãjiri mai yawan kãfirci"

:28

"Ya Ubanginjina! Ka yi mini gãfara (ni) da mahaifana biyu, da wanda ya shiga gidana, yana mai ĩmãni, da mũminai maza da mũminai mãtã, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai kõme sai halaka."