All Islam Library

69 - The Reality - Al-Ĥāqqah

:1

Kiran gaskiya!

:2

Mẽne ne kiran gaskiya?

:3

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?

:4

Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!

:5

To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.

:6

Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.

:7

(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.

:8

To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?

:9

Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.

:10

Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).

:11

Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.

:12

Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

:13

To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.

:14

Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.

:15

A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.

:16

Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.

:17

Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.

:18

A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.

:19

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."

:20

"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."

:21

Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.

:22

A cikin Aljanna maɗaukakiya.

:23

Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),

:24

(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."

:25

Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"

:26

"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"

:27

"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!

:28

"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"

:29

"Ĩkona ya ɓace mini!"

:30

(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."

:31

"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."

:32

"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."

:33

"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"

:34

"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"

:35

"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."

:36

"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."

:37

"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."

:38

To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,

:39

Da abin da bã ku iya gani.

:40

Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

:41

Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.

:42

Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.

:43

Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.

:44

Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.

:45

Dã Mun kãma shi da dãma.

:46

sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.

:47

Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.

:48

Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

:49

Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.

:50

Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.

:51

Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.

:52

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.