All Islam Library

68 - The Pen - Al-Qalam

:1

Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.

:2

Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.

:3

Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.

:4

Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.

:5

Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.

:6

Ga wanenku haukã take.

:7

Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.

:8

Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.

:9

Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.

:10

Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.

:11

Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.

:12

Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.

:13

Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).

:14

Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.

:15

Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."

:16

Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.

:17

Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.

:18

Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.

:19

Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.

:20

Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.

:21

Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.

:22

Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.

:23

Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).

:24

"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"

:25

Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.

:26

Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"

:27

"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."

:28

Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"

:29

Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."

:30

Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.

:31

Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."

:32

"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."

:33

Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.

:34

Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.

:35

Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?

:36

Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?

:37

Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?

:38

Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?

:39

Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?

:40

Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?

:41

Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.

:42

Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.

:43

Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).

:44

Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.

:45

Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.

:46

Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?

:47

Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?

:48

Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.

:49

Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.

:50

Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.

:51

Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"

:52

Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.