All Islam Library
1

Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

2

Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

3

Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

4

A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

5

cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

6

A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

7

To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

8

Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.