All Islam Library

99 - The Earthquake - Az-Zalzalah

:1

Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

:2

Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

:3

Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

:4

A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

:5

cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

:6

A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

:7

To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

:8

Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.