All Islam Library

56 - The Inevitable - Al-Wāqi`ah

:1

Idan mai aukuwa ta auku.

:2

Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.

:3

(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.

:4

Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.

:5

Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.

:6

Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.

:7

Kuma kun kasance nau'i uku.

:8

Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

:9

Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?

:10

Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,

:11

Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.

:12

A ckin Aljannar ni'ima.

:13

Jama'a ne daga mutãnen farko.

:14

Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.

:15

(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.

:16

Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.

:17

Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.

:18

Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.

:19

Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.

:20

Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.

:21

Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.

:22

Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.

:23

Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.

:24

A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.

:25

Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.

:26

Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.

:27

Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?

:28

(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.

:29

Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.

:30

Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.

:31

Da wani ruwa mai gudãna.

:32

Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.

:33

Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.

:34

Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.

:35

Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.

:36

Sa'an nan Muka sanya su budurwai.

:37

Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.

:38

Ga mazõwa dãma.

:39

Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.

:40

Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.

:41

Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?

:42

Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.

:43

Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.

:44

Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.

:45

Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.

:46

Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.

:47

Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"

:48

"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"

:49

Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."

:50

"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."

:51

"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"

:52

"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."

:53

"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."

:54

"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."

:55

"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."

:56

Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.

:57

Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?

:58

Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?

:59

Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?

:60

Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,

:61

A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.

:62

Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?

:63

Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?

:64

Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?

:65

Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.

:66

(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"

:67

"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"

:68

Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?

:69

Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?

:70

Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?

:71

Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?

:72

Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?

:73

Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.

:74

Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.

:75

To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.

:76

Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.

:77

Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.

:78

A cikin wani littafi tsararre.

:79

Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.

:80

Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.

:81

Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?

:82

Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?

:83

To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).

:84

Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.

:85

Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.

:86

To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?

:87

Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.

:88

To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,

:89

Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.

:90

Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,

:91

Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.

:92

Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,

:93

Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.

:94

Da ƙõnuwa da Jahĩm,

:95

Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.

:96

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.