All Islam Library

54 - The Moon - Al-Qamar

:1

Sã'a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge.

:2

Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"

:3

Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.

:4

Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.

:5

Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.

:6

Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.

:7

¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.

:8

Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"

:9

Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.

:10

Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."

:11

Sai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba.

:12

Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi.

:13

Kuma Muka ɗauke Nũhu a kan (jirgi) na alluna da ƙũsõshi.

:14

Tanã gudãna, a kan idãnunMu, dõmin sakamako ga wanda aka yi wa kãfircin.

:15

Kuma lalle, Mun bar ta ta zama ãyã. To, Shin, akwai mai tunãni

:16

To, yãyã azãbãTa take da gargaɗiNa?

:17

Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

:18

Ãdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗiNa?

:19

Lalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.

:20

Tanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.

:21

To, yãya azãbãTa take da gargaɗiNa?

:22

Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

:23

Samũdãwa sun ƙaryata game da gargaɗin.

:24

Sai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bĩ shi! Lalle mũ a lõkacin, haƙĩƙa mun shiga wata ɓata da haukã.

:25

"Shin, an jẽfa masa Manzancin ne, a tsakãninmu? Ã'a, shĩ dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai!"

:26

Zã su sani a gõbe, wãne ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan?

:27

Lalle Mũ, mãsu aikãwa da rãƙumar ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri.

:28

Kuma ka bã su lãbãri cẽwa ruwa rababbe ne a tsakãninsu (da rãƙumar), kõwane sha, mai shi yanã halartar sa.

:29

Sai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa'an nan ya sõke ta,

:30

To, yãya azãbaTa take da gargaɗiNa?

:31

Lalle Mũ, Mun aika tsãwa guda a kansu, sai suka kasance kamar yãyin mai shinge.

:32

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

:33

Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi.

:34

Lalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, fãce mabiyan Lũɗu, Mun tsirar da su a lõkacin asuba.

:35

Sabõda wata ni'ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke sãka wa wanda ya gõde.

:36

Kuma lalle, haƙĩƙa, ya yi musu gargaɗin damƙarMu, sai suka yi musu game da gargaɗin.

:37

Kuma lalle haƙĩƙa, su, sun nẽme shi ta wajen bãƙinsa, sai Muka shãfe idãnunsu. "To, ku ɗanɗani azãbaTa da gargaɗĩNa."

:38

Kuma lalle, haƙĩƙa, wata azãba matabbaciya tã wãye musu gari da yãƙi, tun da sãfe.

:39

To, ku ɗanɗani azãbãTa da gargaɗĩNa.

:40

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

:41

Kuma lalle, haƙĩƙa, gargaɗin ya jẽ wa mabiyan Fir'auna.

:42

Sun ƙaryata game da ãyõyinMu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi.

:43

Shin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã'a a cikin littattafai?

:44

Kõ zã su ce: "Mũ duka mãsu haɗa ƙarfi ne dõmin cin nasara?"

:45

Zã a karya tãron, kuma su jũya bãya dõmin gudu.

:46

Ã'a, Sã'a ita cẽ lõkacin wa'adinsu, kuma Sã'ar tã fi tsananin masĩfa, kuma ta fiɗãci.

:47

Lalle ne, mãsu laifi sunã a cikin ɓata da hauka.

:48

Rãnar da zã a jã su a cikin wuta a kan fuskõkinsu. "Ku ɗanɗani shãfar wutar Saƙar."

:49

Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri.

:50

Kuma umurninMu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.

:51

Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?

:52

Kuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.

:53

Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.

:54

Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.

:55

A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.