All Islam Library
1

Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba?

2

Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba?

3

Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.

4

Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.

5

Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?