All Islam Library
1

Bone ya tabbata ga duk mai nune, mai zunɗe (mai raɗa).

2

Wanda ya tara dũkiya, kuma ya mayar da ita abar tattalinsa.

3

Yana zaton cẽwa dũkiyarsa za ta dawwamar da shi.

4

A'aha! Lalle ne zã a jẽfa shi a cikin Huɗama.

5

Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa Huɗama?

6

Wutar Allah ce wadda ake hurawa.

7

Wadda take lẽƙãwa a kan zukata.

8

Lalle ne ita abar kullẽwa cea kansu.

9

A cikin wasu ginshiƙai mĩƙaƙƙu.