All Islam Library

75 - The Resurrection - Al-Qiyāmah

:1

Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.

:2

Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.

:3

Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?

:4

Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.

:5

Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.

:6

Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"

:7

To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).

:8

Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

:9

Aka tãra rãnã da watã

:10

Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"

:11

A'aha! bãbu mafaka.

:12

zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.

:13

Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.

:14

Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.

:15

Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).

:16

Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).

:17

Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.

:18

To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.

:19

sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.

:20

A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.

:21

Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).

:22

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.

:23

Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.

:24

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.

:25

Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.

:26

A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.

:27

kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"

:28

Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.

:29

Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.

:30

Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.

:31

To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!

:32

Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!

:33

Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.

:34

Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.

:35

Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.

:36

Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?

:37

Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)

:38

Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;

:39

Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?

:40

Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?