All Islam Library

51 - The Winnowing Winds - Adh-Dhāriyāt

:1

Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.

:2

Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).

:3

Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.

:4

Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).

:5

Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.

:6

Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne

:7

Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).

:8

Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).

:9

Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).

:10

An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.

:11

Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.

:12

Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"

:13

Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.

:14

(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."

:15

Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.

:16

Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).

:17

Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.

:18

Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.

:19

Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.

:20

Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.

:21

Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?

:22

Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.

:23

To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,

:24

Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?

:25

A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"

:26

Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,

:27

Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"

:28

Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.

:29

Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"

:30

Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."

:31

(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"

:32

Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.

:33

"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).

:34

"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."

:35

Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.

:36

Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.

:37

Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.

:38

Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.

:39

Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"

:40

Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

:41

Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.

:42

Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.

:43

Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"

:44

Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.

:45

Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.

:46

Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.

:47

Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.

:48

Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,

:49

Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.

:50

Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

:51

Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

:52

Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."

:53

shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.

:54

Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.

:55

Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.

:56

Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.

:57

Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.

:58

Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.

:59

To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.

:60

Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.