All Islam Library

37 - Those who set the Ranks - Aş-Şāffāt

:1

Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).

:2

Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.

:3

Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.

:4

Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.

:5

Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.

:6

Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.

:7

Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.

:8

Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.

:9

Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.

:10

Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.

:11

Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.

:12

Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.

:13

Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.

:14

Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.

:15

Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."

:16

"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?

:17

"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"

:18

Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."

:19

Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.

:20

Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."

:21

Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.

:22

Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.

:23

Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.

:24

Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.

:25

Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?

:26

Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.

:27

Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.

:28

Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."

:29

Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.

:30

"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."

:31

"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."

:32

"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."

:33

To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.

:34

Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.

:35

Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.

:36

Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?

:37

Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.

:38

Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.

:39

Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.

:40

Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

:41

Waɗannan sunã da abinci sananne.

:42

'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.

:43

A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.

:44

A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.

:45

Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.

:46

Farã mai dãɗi ga mashãyan.

:47

A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,

:48

Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.

:49

Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.

:50

Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.

:51

Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."

:52

Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"

:53

"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"

:54

(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"

:55

Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.

:56

Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."

:57

"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."

:58

"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."

:59

"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"

:60

Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.

:61

Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.

:62

Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?

:63

Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.

:64

Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.

:65

Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.

:66

To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.

:67

Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.

:68

Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.

:69

Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.

:70

Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.

:71

Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.

:72

Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.

:73

Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.

:74

Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

:75

Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.

:76

Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.

:77

Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.

:78

Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.

:79

Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.

:80

Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

:81

Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.

:82

Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.

:83

Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.

:84

A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.

:85

A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"

:86

"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"

:87

"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"

:88

Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.

:89

Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."

:90

Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.

:91

Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?

:92

"Me ya sãme ku, bã ku magana?"

:93

Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.

:94

Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.

:95

Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,

:96

"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"

:97

Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."

:98

Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.

:99

Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."

:100

"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."

:101

Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.

:102

To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."

:103

To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.

:104

Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"

:105

"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

:106

Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.

:107

Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.

:108

Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.

:109

Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.

:110

Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

:111

Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

:112

Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.

:113

Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).

:114

Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.

:115

Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.

:116

Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.

:117

Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.

:118

Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.

:119

Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.

:120

Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.

:121

Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

:122

Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.

:123

Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

:124

A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"

:125

"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"

:126

"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"

:127

Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).

:128

Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

:129

Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.

:130

Aminci ya tabbata ga Ilyãs.

:131

Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

:132

Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

:133

Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

:134

A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.

:135

Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).

:136

Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.

:137

Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.

:138

Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?

:139

Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

:140

A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.

:141

Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.

:142

Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

:143

To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,

:144

Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.

:145

Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.

:146

Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.

:147

Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).

:148

Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.

:149

Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"

:150

Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?

:151

To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.

:152

"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.

:153

Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?

:154

Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?

:155

Shin, bã ku tunãni?

:156

Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?

:157

To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.

:158

Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"

:159

Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.

:160

Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

:161

To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,

:162

Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.

:163

Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.

:164

"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."

:165

"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."

:166

"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."

:167

Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,

:168

"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."

:169

"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."

:170

Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.

:171

Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.

:172

Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.

:173

Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.

:174

Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.

:175

Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.

:176

Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?

:177

To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.

:178

Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.

:179

Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.

:180

Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.

:181

Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.

:182

Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.